Wasu magidanta su biyu sun dambace kuma suka yi wa juna dukan tsiya har da barnata motar daya daga cikinsu saboda wata mata a Makurdi babban birnin jihar Benue. Shafin labarai na isyaku.com ya ruwaito.
Lamarin ya faru ne ranar Talata 31 ga watan Agusta 2021.
Wani ganau mai suna Atsuwe Shadrack, ya ce magidantan sun ba hammata iska ne saboda wata mata a kusa da babban kasuwar kasa da kasa a birnin Makirdi.
Sai dai bai yi bayani da musabba in lamarin ba.