'Miljyoyin yan Najeriya na rayuwa cikin matsananciyar yunwa'


BBC Hausa ta ruwaito cewa kimanin mutum miliyan 4.4 ne ke rayuwa cikin matsananciyar yunwa a arewa maso gabashin Najeriya saboda hare-haren mayakan Boko Haram wadanda suka hana noma aiki, in ji Majalisar Dinkin Duniya.

Yankin dai na fama da matsalar tsaro na sama da shekara 20, MDD ta ce hakan zai iya kai wa ga rashin abin ci a yankin.

Mace-macen da aka samu sakamakon rikicin da kuma matsalar annobar korona sun ƙara ta'azzara lamarin.

Quote Message: Hukumomi a Najeriya ya kamata su haɗa hannu da kungiyoyin da ke aikin ba da agaji domin shawo kan wannan matsala ta ƙarancin abinci, in ji babban jami'n ayyukan agaji na MDD a Najeriya Edward Kallon

Masu kai hare-hare dai sun fi kai wa manoma a yankin arewa maso gashin da nufin daƙile samar da abinci.

Bugu da ƙari hare-haren nasu na ƙarasa wa har kan jami'an tsaron Najeriya a yankin.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN