Maigida ya lafta wa matarsa dukar kutufo har da zubar mata da jini a garin Birnin kebbi


Wani magidanci ya yi wa matarsa dan karen duka har da rauni da ya zubar da jini a Unguwar bayan Oando da ke garin Birnin kebbi.S

Shafin isyaku.com ya samo cewa, rigima ce ta barke tsakanin miji da matarsa da misalin karfe 10 na safe ranar Asabar. Sakamakon haka mijin matar ya yi mata laga laga da duka har da raunuka da suka fitar da jini.

Mun samo cewa mijin matar wanda ma'aikacin gwamnati ne a daya daga cikin ma'aikatun da ke Sakatariyar Haliru Abdu, ya sha yi wa matarsa mugun duka, kuma an yi zargin cewa yakan yi barazanar cewa idan ya kasheta ya kashe banza, sai dai ya yi hursuna.

Kazalika wata majiya makusanciya ga iyalin, ya shaida mana cewa ma'auratan sun shafe shekara 20 tare, har da samun albarkar haihuwar yara 7. 

Ya ce ba wannan ne karo na farko da mijin matar yake yi mata duka ba. Kuma ya ce surukanshi na daga masa kafa ne saboda zuriar yara 7 da Allah ya basu.

Mun samo cewa zancen na gaban jami'an tsaro a halin yanzu. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN