Labarin kashe 'yan ƙabilar Igbo 230 a Jos ba gaskiya ba ne - 'Yan sanda


Rundunar 'yan sandan Jihar Filato ta bayyana rahoton da ke cewa wasu mahara sun kashe mutum 230 'yan ƙabilar Igbo a Jos a matsayin labarin ƙarya.

Kakakin rundunar, ASP Ubah Ogaba, shi ne ya musanta rahoton cikin wata sanarwa a ranar Lahadi.

Rahotanni sun karaɗe shafukan zumunta cewa maharan sun cinna wa wa motocin bas da ke ɗauke da mutanen 'yan ƙabilar Igbo wuta, inda suka kashe 230.

Mista Ogaba ya jaddada cewa lbarin ba shi da ƙanshin gaskiya sannan ya nemi mutane da su guji yaɗa shi.

Lamarin na zuwa ne bayan rikicin ƙabilanci ya yi sanadiyyar kashe mutum kusan 30 a garin Yelwan Zangam a makon da ya gabata. Kazalika, wasu mahara sun tare wa matafiya hanya tare da kashe 27 mako uku da suka wuce a Jos.

Rahotun BBC Hausa

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN