Duba abinda ya faru bayan Malam Abduljabbar Nasir Kabara ya sake gurfana kotu


Malam Abduljabbar Nasir Kabara ya sake gurfana gaban kotu a Kano kan laifukan da ake tuhumarsa na yin kalaman tunzura jama'a da É“atanci ga addinin Islama. Zargin da ya sha musantawa,  BBC Hausa ta ruwaito a shafinta.

A ranar 30 ga watan Yulin da ya gabata aka fara gurfanar da Abduljabbar Nasir Kabara, inda aka gabatar da takardar korafin farko.

Gwamnatin Kano ta ce ta gurfanar da Malamin ne, wanda ta ce ya yi ƙaurin suna wajen yin wa'azin da kan haifar da mahawara, saboda zargin furta kalaman da ka iya haifar da tunzuri, da kuma bata sunan Annabin Allah''.

Wakilin BBC da ke cikin kotun da ake sauraren ƙarar Malam Abduljabbar ya ce an tsaurara tsaro fiye da zaman kotun da aka yi a farko.

Ya kuma ce Malam Abduljabbar a ya rame a yanayin yadda ya bayyana a sauraren ƙararsa da ake yi a kotun a ranar Laraba.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN