Rahotanni daga jihar Niger sun ce yan bindigan da suka sace Muhammed
Sanni Idris, sun nemi a biya su N500 kafin su sake shi. Shafin isyaku.com ya ruwaito.
Yan bindigan sun sace Kwamishinan ne a kauyensu da ke Baban Tunga a karamar hukumar
Tafa ranar Litinin 9 ga watan Agusta.
Bayanai sun ce tun safiyar Litinin ake ta ganawa kan lamarin karkashin jagorancin Mataimakin Gwamnan jihar Niger Ahmed Ketso.
Wata majiya ta gaya wa Daily Trust cewa yan bindigan sun tuntubi iyalinsa kuma sun bukaci a basu kudaden fansar har N500m.Sai dai har yanzu babu tabbacin bukatar da yan bindigan suka yi ga iyalin Kwamishinan daga jami'an tsaro ko mahukunta a jihar Niger.