Da duminsa: Yan bindiga sun sace wani shugaban jam'iyar APC a jihar arewa


Wasu Yan bindiga sun sace Mallam Aminu Bobi, wani tsohon shugaban jam'iyar All Progressives Congress (APC)  Zone ‘C’ a jihar Niger. Jaridar Legit ta ruwaito.

The Nation ta ruwaito cewa Yan bindigan sun sace Bobi ne ranar Asabar 7 ga watan Agusta da misalin karfe 5 na yamma lokacin da ya je duba wani aiki da ake yi a gonarsa da ke karamar hukumar Mariga a jihar Niger.

Wani ganau ya ce Yan bindigan su 18 kan babura 6 sun shiga gonar ne suka yi ta harbin mai uwa da wabi a iska kuma suka dauke shugaban na APC shi kadai suka bar sauran ma'aikatan da ke aiki a gonar.

A lokacin rubuta wannan rahotu, Kakakin hukumar yansandan jihar Niger DSP Abiodun Wasiu bai tabbatar da faruwar lamarin ba kafin yanzu. 

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN