Da Dumi-Dumi: Malamai da Dalibin Kwalejin Zamfara Sun tsero Daga Hannun Yan bindiga


Malamai biyu da É—alibi É—aya daga cikin waÉ—anda aka sace a kwalejin Noma dake Bakuri, jihar Zamfara sun tsero daga hannun yan bindiga, kamar yadda punch ta ruwaito.

Mataimakin shugaban kwalejin, Ali Atiku, shine ya bayyana haka ga manema labarai ranar Litinin.

Atiku Yace:

"Biyu daga cikin malamai da kuma É—alibi É—aya sun tsero daga hannun yan bindiga bayan sun sace su, sun komo makaranta da safiyar Litinin.

"Zuwa yanzun da nake magana da ku mun gano cewa maharan sun sace É—alibai 15 duk maza, sai kuma malamai nata uku da namiji É—aya, kuma sun kashe jami'an tsaron mu guda biyu."

Me hukumar yan sanda tace game da lamarin?

Har zuwa yanzun da muke kawo muku wannan rahoton hukumar yan sanda reshen jihar Zamfara ba tace uffan ba game da lamarin.

A baya, yan bindiga sun taba sace shugaban kwalejin aikin noma dake Bakura, Alhaji Habibu Mainasara

Sai dai daga baya É“arayin da suka yo garkuwan da shi sun sako shi bayan an biyasu kuÉ—in fansa

Source: Legit

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN