An cafke wasu mutane uku bayan sun sace wata mata suka nemi kudin fansa a yankin Ogombo/Lekki Ajah a jihar Lagos.
Jami'an yansanda sashen Intelligence Response Team na ofishin yansanda da ke Ogombo a jihar Lagos ne suka kama mutanen bayan sun bukaci a biya su N500m kafin su saki matar da suka kama.
CSP Adekunle Ajisebutu, shi ne Kakakin hukumar yansandan jihar Lagos, ya tabbatar da faruwar lamarin. Ya ce an kuɓutar da wacce aka kma kuma ta koma cikin iyalinta.
Ya ce an mika masu garkuwan zuwa sashen binciken kwakwaf na CID domin ci gaba da bincike.