An damke barawon manyan wayoyin wuyar lantarki a jihar Arewa


Rundunar yansandan jihar Adamawa ta kama wani matashi mai suna Haruna  Muhammed mai shekara 29 bisa zargin satar manyan wayoyin wutan lantarki a karamar hukumar Mubi ta kudu.

Kakakin hukumar yansandan jihar DSP Suleiman Nguroje ya ce an kama Haruna wanda dan asalin Angwan Kara a Mubi ta kudu ne bayan ya aikata satan kuma ya je ya boye a maboyarsa da ke Mugulvu a bayan wata Makabarta yana jiran abokan harkallarsa.

Sakamkon harkar sace sacen wayoyin lantarki da Haruna da abokan harkallarsa ke yi ya sa suka jefa jama'ar Maiha, Mubi da garuruwa da ke makwabtaka cikin matsalar wutan lantarki.

Yansanda na ci gaba da gudanar da bincike kuma za su maka Haruna a wata Kotu domin ya fuskanci hukunci a cewar Kakakin rundunar yansandan jihar Adamawa. 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN