Allah ya yi wa mahaifiyar marigayi Ibrahim Abdulazeez Wakilin Muryar Amurka mai suna Hajiya Biba rasuwa. An fi saninta da suna Mamman.
Ta rasu a garin Mayo Belwa da safiyar Asabar 3 ga watan Yuli, 2021.
Za a yi jana'izarta a garin Mayo Belwa na jihar Adamawa.
Marigayi Ibrahim Abdulazeez, shahararren Dan Jarida ne Wanda ya wakilci gidan rediyon Muryar Amurka a jihohin Adamawa, Bauchi da Gombe, ya rasu cikin watan Fabrairu na wannan shekarar, wata biyar tsakanin rasuwarsa da rasuwar mahaifiyarsa ranar Asabar.
Amadadin dukkan ma'aikatan shafin labarai na ISYAKU.COM, Malam Isyaku Garba Zuru, Mawallafin shafin, yana isar da ta'aziyyarsu ga iyalai, yan'uwa da abokan arziki ga marigayi Ibrahim. Tare da fatar Allah ya gafarta masa tare da mahaifiyarsa ya amshi bakoncinsu kuma ya hore masu Aljannah. Ya sa mu cika da Imani tare da yin kyakkyawan karshe. Amin.