Yanzu yanzu: Allah ya yi wa mahaifiyar Ibrahim Abdulazeez na muryar Amurka rasuwa


Allah ya yi wa mahaifiyar marigayi Ibrahim Abdulazeez Wakilin Muryar Amurka mai suna Hajiya Biba rasuwa. An fi saninta da suna Mamman.

Ta rasu a garin Mayo Belwa da safiyar Asabar 3 ga watan Yuli, 2021. 

Za a yi jana'izarta a garin Mayo Belwa na jihar Adamawa.


Marigayi Ibrahim Abdulazeez, shahararren Dan Jarida ne Wanda ya wakilci gidan rediyon Muryar Amurka a jihohin Adamawa, Bauchi da Gombe, ya rasu cikin watan Fabrairu na wannan shekarar, wata biyar tsakanin rasuwarsa da rasuwar mahaifiyarsa ranar Asabar.

Amadadin dukkan ma'aikatan shafin labarai na ISYAKU.COM, Malam Isyaku Garba Zuru, Mawallafin shafin, yana isar da ta'aziyyarsu ga iyalai, yan'uwa da abokan arziki ga marigayi Ibrahim. Tare da fatar Allah ya gafarta masa tare da mahaifiyarsa ya amshi bakoncinsu kuma ya hore masu Aljannah. Ya sa mu cika da Imani tare da yin kyakkyawan karshe. Amin. 

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN