Rundunar yansandan jihar Adamawa ta kama wani ma'aikacin gwamnati mai suna Usman Hammawa, mai shekara 41 a Duniya bisa zargin yi wa matarsa mai shekara 36 a Duniya duka har ta mutu,
Kakakin hukumar yansandan jihar Adamawa DSP Suleiman Yahaya Nguroje, ya tabbatar da aukuwan lamarin a wata takarda da ya fitar ga manema labarai. Ya ce an kama wanda ake zargin ne ranar Talata 22 ga watan Yuli a karamar hukumar Ganye.
Ngoroje ya ce Usman Hammawa ya fusata ya fada wa matarsa da duka kuma ya buga kan matarsa mai suna Rabiyatu Usman da bango saboda ta tambaye shi Naira 1000 da take binshi bashi. Usman da Rabiatu sun shafe shekara 16 tare kafin Usman ya zama ajalinta a zamantakewar aurensu.
Sakamakon haka Rabiatu ta fadi ta suma kuma aka garzaya zuwa asibiti da ita inda aka tabbatar da mutuwarta.