Sunday Igboho, mai ikirarin kare hakkin Yarbawa, ya sha alwashin yin gangamin ƙasar Yarbawa da shi da mabiyansa suka shirya yi a Legas a ranar Asabar, Daily Trust ta ruwaito.
Igboho ya sanar da dakatar da gangamin a ranar Laraba bayan da jami'an hukumar DSS suka kai samame gidansa a Ibadan a ranar Laraba.
Amma wani sako na kai tsaye da ya fitar ta shafin Facebook a ranar Alhamis, Igboho ya ce za a yi gangamin kamar yadda The Nation ta ruwaito.
https://www.youtube.com/watch?v=CoxzBKB5JJA
Source: Legit.ng