Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi alhinin mutuwar dan majalisar Zamfara


An tattaro cewa yan bindigan sun kuma yi awon gaba da yaron dan majalisar da kuma direbansa.

Shugaba Buhari, a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Garba Shehu ya saki a ranar Alhamis, 1 ga watan Yuli, ya nuna alhinin rasuwar dan siyasar, kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya ruwaito.

Shugaban kasar ya roki Allah Ya ji kan marigayin Ya sa ya huta. Ya kuma yi addu'ar Allah ya ba duk wadanda ke alhinin mutuwar mamacin juriya na wannan babban rashi.

Shugaban na Najeriya ya ci gaba da nanata umarnin da ya ba hukumomin tsaro na yin maganin miyagu da ke son cutar da 'yan kasa da basu ji ba basu gani ba.

Matawalle Ya Yi Magana Kan Kisan ÆŠan Majalisar Jiharsa, Ya Bayyana Alhininsa

A baya mun ji cewa Gwamna Matawalle na jihar Zamfara, ya nuna kaÉ—uwarsa kan kisan É—an majalisar dokokin jihar mai wakiltar Shinkafi, Alhaji Muhammed G. Ahmed, wanda yan bindiga suka kashe ranar Talata da daddare, kamar yadda leadership ta ruwaito.

A wani jawabi da kakakin gwamnan, Yusuf Idris Gusau, ya fitar, gwamnan ya bayyana marigayin a matsayin mutumin kirki kuma mai juriya.

Matawalle yace yaji labari mara daɗi na mutuwarsa kuma ya kaɗu matuƙa saboda marigayin yana tare da shi kwana ɗaya kafin faruwar lamarin yayin sauya shekarsa zuwa APC.

Source: Legit.ng

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN