Mutum 9 'yan gida daya sun sheka lahira bayan cin abinci mai guba a Zamfara


Tashin hankali ya fada kauyen Jangeme dake karamar hukumar Gusau ta jihar Zamfara lokacin da wasu 'yan gida daya suka sheka lahira bayan cin guba da suka yi a abinci.

Wani kawun mamatan mai suna Abdullahi Bello ya sanar da Daily Trust cewa yaran sun mutu ne bayan 'yar uwarsu da ta kawo musu ziyara daga gidan mijinta ta yi musu Tuwon dawa.

Bello ya ce: "Yayin da ta zo gida, ta debo dawa daga rumbu kuma ta kai nika. Wani beran masar da ake kiwo a gidan ya mutu bayan ya ci garin tun kafin ta fara yin tuwon.

"Babu wanda ya gano cewa akwai guba a garin ko batan da beran masar din ya mutu. Ta yi girkin kuma yaran sun ci. Bayan sa'o'i kadan yaro daya ya mutu.

"Daga nan muka kwashi yaran muka mika su asibiti a Gusau inda wasu biyu suka mutu. bayan mun kwashi gawarsu muna birnesu ne aka kira mu cewa wasu uku sun mutu, ciki har da wacce tayi girkin. A takaice dai 'ya'ya takwas tare da mahaifiyarsu suka mutu."

A yayin da aka kai ziyara asibitin Yariman Bakura dake Gusau, Daily Trust ta ga yaro daya daga cikin wadanda suka ci tuwon rai a hannun Allah.

"Tabbas likitoci sun tabbatar da cewa lamarin ya fara ne bayan sun ci abinci mai guba," mai magana da yawun hukumar asibitin, Awwal Usman Ruwan Dorawa ya sanar.

Ya ce likitocin sun yi kokarin ceto rayukan yaran amma matasalar ita ce ba a mika su asibiti da wuri ba.

Gwamnatin tarayya ta yi shiru kuma bata sanar da inda ta kama Kanu ba, lamarin da yasa ake ta cece-kuce, Daily Trust ta ruwaito.

Amma a wata takarda da ya fitar a ranar Laraba, Kingsley ya ce hukumomin kasar Kenya sun kama dan uwanshi har sai da hukumomin tsaro na Najeriya suka je suka taso keyarsa.

Rahotun Legit

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN