Kotun Najeriya ta yankewa wasu tsoffin ‘yan sanda biyu hukuncin kisa saboda garkuwa da wani abbar kotun jihar Akwa Ibom ta yanke wa wasu ‘yan sanda biyu hukuncin kisa saboda yin garkuwa da wani dillalin shanu mazaunin Uyo, mai suna Alhaji Muhammed Umar Barkindo.
‘Yan sandan da aka yanke wa hukuncin sun hada da Kofur Friday Udo, da kuma Saturday Okorie wadanda tuni aka sallame su daga rundunar ‘yan sanda ta Najeriya, jaridar The Punch ta ruwaito.
Kotun da ke zaune a karamar hukumar Ikot Ekpene ta jihar ta kuma yanke hukuncin kisa ga wasu mutum uku, Walter Udo, Ibiono Ibom, da Udo Etim wadanda aka yi amfani da gidansu don ajiye wanda aka yi garkuwa da shi, yayin da suke neman fansar naira miliyan 100
Rahotun Legit