Rundunar yansandan jihar Cross River ta kama wani Pasto bisa zargin mallakan kwarangwam kan Dan Adam ba tare da izini ba.
Kwamishinan yansandan jihar Mr Sikiru Akande ya ce an kama wanda ake zargin ne a gida mai lamba 56 a Uwanse, kusa da unguwar Asuquo Ekpo a Calabar ta kudu.
Akande ya ce;
"An kama Paston ne da kwarangwam kan Dan Adam da aka sassaka daure da hoton wanda ya yi kara a kansa. Tare da wani jar kelle da aka lullube hadi da wasu kayakin tsafi"
Sai da wanda aka kama ya musanta cewa shi bai san komai ba dangane da larin kwarangwam kan Dan Adam. Ya ce shi ba matsafi bane illa mai warkar da jama'a daga sihiri ko sammu da aka yi masu".