Gwamna Ganduje Ya Dakatar da Kungiyar Masu Bashi Shawari Na Musamman Saboda Rikicin Cikin gida


Gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya dakatar da kungiyar manyan mataimaka ta musamman a Kano saboda rikicin shugabanci, Daily Trust ta ruwaito.

Gwamnan, a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Usman Alhaji, ya ce gwammnati ta lura cewa abubuwan dake gudana a kungiyar suna dauke musu hankali daga asalin ayyukansu da kuma ba da gudunmawarsu ga gwamnati.

Ya ce rashin jituwar da ke tsakanin shugabannin biyu na kungiyar ya haifar da rashin jin dadi da kunya ga gwamnati wanda in ba a kula ba, za ta iya lalata manufofi da burin da aka sanya kan SSA din.

Source: Legit News

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN