Da duminsa: Yan bindigan sun sace Manajan SRRBDA na garin Dutsin-Ma a jihar Katsina


Yan bindigan sun sace Manajan Sokoto Rima River Basin Development Authority (SRRBDA), na yankin Dutsin-Ma, Labaran Muhammed Dandume cikin daren ranar Alhamis, OBSERVERS TIMES ta ruwaito.

Wata majiya a Dutsin-Ma ta ce mutanen sun dauke Manajan ne a gidansa da ke gidajen SRRBDA da misalin karfe 11:47 na dare ranar Alhamis. 

Duk da yake an sami mabanbantan bayanai kan Labarin yadda Yan bindigan suka sace Manajan a samame da Yan bindigan suka gudanar a kasa da minti 20.

Kakakin hukumar yansandan jihar Katsina SP Gambo Isah, ya ce Yana sane da faruwar lamarin. Sai dai ya ce a bashi lokaci domin tattara bayanai kafin ya yi bayani kan lamarin.

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN