Yan bindigan daji sun kutsa cikin gidan Sarkin Kajuru Alhaji Hassan Adamu suka dauke shi a karamar hukumar Kajuru na jihar Kaduna. Daily Trust ta ruwaito.
Kazalika Yan bindigan sun yi awon gaba da mutum 12 cikin iyalinsa da suka hada da mata da yara.
Wani jikan basaraken wanda kuma shi ne ke rike da mukamin Dan Kajuru, Sa'idu Musa ya tabbatar wa Wakilin Daily trust da faruwar Lamarin .
Ya ce lamarin ya faru da misalin karfe 12:30 na dare.
Cikakken labari anjima.......