Wani mazaunin garin mai suna Kabir Dansada ya fada wa Daily Trust cewa:
“Sun janye bayan da sojojin dake wurin suka ci karfinsu. Daga nan suka yi tattaki zuwa wata al'umma dake kan hanyar Magami - Dankurmi - Dangulbi suka kashe mutum daya kuma suka kone shaguna hudu.”
“Daga baya, sai suka koma garin Kurar Mota kuma suka kai hari kan sansanin 'yan sanda kusa da asibitin garin. Daga nan sai 'yan ta'addan suka fantsama cikin daji ”
“An kai jami’an da aka kashe da wadanda suka jikkata zuwa Gusau a cikin ayarin motocin 'yan sanda da yammacin yau. Na ga motocin ‘yan sanda da dama suna zirga-zirga zuwa yankin."
Har yanzu ba ji ta bakin 'yan sanda ba, duk da cewa an tuntubi kakakin rundunar 'yan sandan jihar SP Muhammad Shehu.
Rahotun BBC