Usman Alkali Baba, Sufeto-Janar na ’Yan sanda (IGP), ya ba da umarnin aikawa tare da sauyawa mataimakan Sufeto-Janar na 'Yan sanda 24 (AIGs) mukamai da kuma wuraren aiki na shiyyoyi.
A cewar wata sanarwa da Legit.ng ta samo a ranar Talata, 27 ga watan Yuli, ta bakin kakakin rundunar ‘yan sanda, CP Frank Mba, sauya wuraren aikin ya dace da sabuwar manufar ci gaban 'Yan Sandan Najeriya.
Sanarwar ta nuna cewa AIG Bala Ciroma zai koma shiyya ta 7 Abuja yayin da AIG Usman Belel, AIG John Amadi da AIG Adeleke Adeyinka aka tura su zuwa FCID Annex Lagos, Maritime da shiyya ta 9 da ke Umuahia bi da bi.
Jerin Jami'an 'Yan Sanda da IGP ya tura jihohin Najeriya baki daya
Ga jerin sunayensu:
AIG SPU FHQ Abuja - AI Zaki M. Ahmed
AIG Shiyya ta 4 Makurdi - AIG Mustapha Dandaura
AIG CTU FHQ Abuja - AIG Dansuki D. Galadanchi, mni
AIG Shiyya ta 17 Akure - AIG Okon Etim Ene, mni
AIG 'Yan Sintiri FHQ Abuja - AIG Usman D. Nagogo
AIG Shiyya ta 7 Abuja - AIG Bala Ciroma
AIG Shiyya ta 9 Umuahia - AIG Adeleke Adeyinka Bode
AIG Shiyya ta 13 Ukpo-Dunukofia Awka - AIG Muri Umar Musa
Kwamanda Polac Wudil-Kano - AIG Lawal Jimeta Tanko
AIG FCID Annex Lagos - AIG Usman AlHassan Belel
AIG DOPS FHQ Abuja - AIG Adebola Emmanuel Longe
AIG Sashen Zuba Jari FHQ Abuja - AIG Musa Adze, fdc
AIG DICT FHQ Abuja - AIG Philip Sule Maku, fdc
AIG Shiyya 6 Calabar - AIG Usman Sule Gomna
AIG Hadin gwiwa - AIG Adamu Usman
AIG Shiyya ta 3 Yola - AIG Daniel Sokari-Pedro, mni
AIG DTD FHQ Abuja - AIG Ahmed Mohammed Azare
AIG FCID Annex Kaduna - AIG Maigana Alhaji Sani
AIG Shiyya ta 12 Bauchi - AIG Audu Adamu Madaki
AIG Maritime Lagos - AIG John Ogbonnaya Amadi, mni
AIG Shiyya ta 8 Lokoja - AIG Ede Ayuba Ekpeji
AIG Armament FHQ Abuja - AIG Mohammed L. Bagega
AIG Shiyya ta 15 Maiduguri - AIG Bello Makwashi
AIG Bangaren ayyuka FHQ Abuja - AIG Balarabe Abubakar
Da Ɗumi-Ɗumi: Sarki Mai Sanda Mai Daraja Ta Ɗaya Ya Rasu a Kaduna
Manufar sauye-sauye da sabbin aikewar
Legit.ng ta tattaro cewa IGP Alkali Baba ya tabbatarwa da kasa cewa aikawar da sauya manyan jami’an 'yan sanda zai kara taimakawa wajen jagorantar sabon hangen nesan 'yan sanda a kasar.
Ya bayyana cewa wannan sabon tsarin na 'yan sanda, a tsakanin sauran abubuwa, an shirya shi ne domin inganta ayyukan 'yan sanda a duk fadin kasar da kuma magance barazanar tsaro a kasar.
A wani labarin, ‘Yan sanda a ranar Litinin sun fatattaki wasu mambobin kungiyar IPOB wadanda suka mamaye Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja don jin yadda za ta kaya a shari’ar Nnamdi Kanu, shugabansu.
Mambobin kungiyar da suka fusata sun mamaye kotun gabanin shari’ar tasa, inda wani rahoton The Cable ya ce tuni an kame wasu daga cikin mambobin na IPOB.
Eid-el-Kabir: Bidiyo ya nuna Buhari yana tafiya zuwa filin Idi a Daura yayin daama'a ke taya shi murna
‘Yan kungiyar IPOB din suna ta rera taken nuna goyon baya ga Kanu tare da neman a sake shi.
Biyu daga cikinsu sun sanya tufafin yahudawa. Wani mutum sanye da bakaken kaya harma yayi wa wasu manema labarai jawabi amma yayi magana ne da yaren Igbo, inji Daily Trust.
Source: Legit.ng