An kammala mukabala: Malam Abduljabbar 'ya kasa amsa dukkanin tambayoyin da aka yi masa'


Alkalin muƙabalar a tsakanin Malam Abduljabbar da malaman Kano ya ce Abduljabbar ya kasa amsa dukkanin tambayoyin aka yi masa.

Alƙalin muƙabalar Farfesa Salisu Shehu shugaban cibiyar addinin Islama da tattaunawa tsakanin addininai ta Jami'ar Bayero ya ce "bisa muƙabalar da aka yi Abduljabbar ya cakuɗa bayanasa, kuma wasunsu ba a kan doron ilimin hadisi yake gina su ba."

"Na yanke hukunci Malam Abduljabbar bai bayar da amsoshin tambayoyin da waɗannan malamai suka yi masa ba," in ji alƙalin muhawarar.

Ya ƙara da cewa babu wata tambaya ɗaya da Abduljabbar ya tunkare ta ya bayar da amsarta.

Kuma ba ya tsayawa kan tambayoyin da aka gabatar masa.

Alƙalin muhawarar ya ce yanzu ya rage ga gwamnati ta yi nazari kan matakin da za ta ɗauka bisa muƙabalar da aka gudanar

Rahotun BBC

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN