Jami'an yan sandan Najeriya sun damke mai daukan hoton Legit TV, Samuel Olubiyo, yayinda yake dauka rahoton zanga-zangan June12 dake gudana a birnin birnin tarayya Abuja.
Mun samu labarin cewa an dauke matashin ne yayinda yake daukan hotunan abubuwan dake gudana a filin zanga-zangan kuma aka kwace kamararsa.
A lokacin kawo muku wannan rahoton, duk wani yunkurin tuntunbarsa da sanin halin da yake ciki ya ci tura.
Wani mai idon shaida ya bayyana mana cewa an damke Samuel ne kuma an kaishe ofishin yans andan Apo duk da cewa ya nuna musu shi dan jarida ne.
Reported by ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari