An kama shugaban kungiyar masu fafutikan kafa kasar Biyafara, Nnamdi Kanu kamar yadda The Cable ta ruwaito.
Amma News Wire ta ruwaito cewa ministan shari'a kuma Attoni Janar, Abubakar Malami ya tabbatarwa da hakan yana mai cewa an kama shi ne ranar Lahadi 27 ga watan Yuni kuma an dawo da shi Nigeria ya fuskanci shari'a.
Ya ce an kama shi ne sakamakon hadin gwiwa tsakanin hukumomin tsaron Nigeria da yan sandan kasa da kasa Interpol.
Malami ya kara da cewa za a gurfanar da Kanu a gaban alkali a babban kotun tarayya Abuja domin cigaba da shari'a da ake masa na tuhumar laifuka da suka shafi cin amanar kasa, mallakar bindiga ba tare da ka'ida ba da kafa kungiya ba bisa ka'ida ba.
Lokacin da aka fara kama Kanu
An fara kama shugaban na kungiyar Indigenous People of Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu ne a watan Oktoban 2015 kan zargin hadin baki wurin aikata laifi da kasancewa mamba na haramtaciyar kungiya.
An bada belinsa kan dalilin rashin lafiya a watan Afrilu amma ba a sake ganinsa ba tun lokacin da sojoji suka kai samame gidansa watanni biyar bayan bada belin.
Kafa kungiyar ESN
A watan Disambar 2020, Kanu ya sanar da cewa ya kafa wata kungiyar tsaro na yankin kudu mai suna ESN. Daga bisani ya bawa gwamonin jihohin kudu wa'adin kwanaki 14 su haramta kiwo a fili.
Ya yi barazanar zai tura jami'an kungiyar ESN su tabbatar da dokar haramta kiwon idan gwamnonin ba za su yi hakan ba.
Rundunar sojojin kasan Nigeria da na sama, a watan Fabrairun wannan shekarar sun fara yi wa yan ESN dirar mikiya sakamakon hare-hare da yan kungiyar ke kaiwa hukumomin gwamnati.
Source: Legit.ng
Reported by ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/L2WpsKOTg5Q6ieoYKEWxeB
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari