Yanzu-Yanzu: Ƴan bindiga sun bindige ɗan majalisar jihar Zamfara har lahira


Yan bindiga sun harbe dan majalisar dokokin jihar Zamfara Mohammed Ahmed har lahira kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Rahotanni sun ce yan bindigan sun kashe Ahmed ne a kan hanyar Sheme zuwa Funtua, wani gari da ke kan iyakar jihar Zamfara da Katsina.

Zamfara da Katsina, jihohin da ke makwabtaka da juna a Arewa maso Yamma na cikin wuraren da yan bindiga suka addaba da hare-hare.

A halin yanzu ba a game bayyana cikaken yadda dan majalisar ya rasu ba amma Saidu Anka, magatakarda a Majalisar dokokin jihar Zamfara ya tabbatar da lamarin a cewar Daily Trust.

An kashe Ahmed ne jim kadan bayan manyan yan siyasa na jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a jihar sun sauya sheka zuwa All Progressives Congress (APC) tare da Gwamna Bello Matawalle.

Ku saurari karin bayani ...

Source: Legit

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN