Yan bindiga sun sace wani jariri ɗan shekara uku tare da mata 5 a Anguwar Epe, bayan sakandiren gwamnati (GSSS) Tungan Maje, Abuja, kamar yadda dailytrust ta ruwaito.
Wani mazaunin yankin mai suna, Ishaku, yace lamarin ya faru da misalin ƙarfe 10:23 na ranar Talata.
Ishaku ya bayyana cewa maharan sun shiga Anguwan cikin dabaru, inda suka fara harbi a sama domin su hana maƙota da jami'an tsaro kawo ɗauki.
Yace: "Yan bindigan sun shigo Anguwan daga jikin wani babban dutse dake bayan Epe, suna zuwa suka raba kansu gida-gida, kafin daga baya wasu tawagar sun kutsa cikin wani gida inda suka yi awon gaba da jariri ɗan shekara 3 da mata 5."
Ya ƙara da cewa kafin jami'an yan sanda su ƙariso yankin tuni yan bindigan sun gama aikin su, sun tafi da waɗanda suka yi niyyar sace wa.
Legit.ng hausa ta gano cewa Tungan-Maje dake kan hanyar zuwa Zuba-Gwagwalada na cigaba da fuskantar matsi daga yan bindiga.
Kakakin hukumar yan sandan Abuja, ASP Maryam Yusuf, ta nemi a tura mata saƙo maimakon kiran waya, amma har yanzun ba ta turo amsar saƙon da aka tura mata ba.
Source: Legit.ng News
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari