Yan bindiga sun sace dalibai da dama a harin Yauri jihar Kebbi


Bayanai daga jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya na cewa wasu 'yan bindiga sun sace dalibai da dama daga Kwalejin Tarayya da ke garin Yawuri.

Ganau sun ce 'yan bindigar sun tafi da dalibai da yawa sannan suka harbi wasu daga cikinsu.

Wani mutum da ya ga lokacin da lamarin ya faru ya gaya wa BBC cewa 'yan bindigar sun ci karfin 'yan sandan da ke gadin makarantar kana suka kwace motoci kirar Toyota Hilux daga wurinsu suka zuba daliban sannan suka tafi da su.

Wasu mutane sun ce an kai dalibai da dama asibiti domin yi musu maganin harbin bindiga sakamakon raunukan da suka samu yayin da suke tserewa daga harin na 'yan bindiga.

Dan majalisar da ke wakiltar yankin a majalisar dokokin tarayya Muhammad Bello Ingaski ya shaida wa BBC cewa 'yan bindigar sun sace dalibai maza da mata da tsakar ranar Alhamis.

'Yan bindigar "sun ci karfin 'yan sandan Mobile da ke gadin makarantar wadanda sun fi 20, sun sassari wasu sannan suka harbi wasu. Akwai 'yan sandan da aka sara an tafi da su asibiti, yayin da su kuma 'yan bindigar suka wuce da wasu yara."

Rahotun BBC

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/L2WpsKOTg5Q6ieoYKEWxeB

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN