Yadda Jirgin Yaƙin NAF Ya Jefa Bam a Wurin Taron Ɗaura Aure a Jihar Neja


A wani harin bam da jirgin rundunar sojin sama ya gudanar a yankin garin Genu, jihar Neja, yayi sanadiyyar mutuwar wasu da suka halarci ɗaurin aure, kamar yadda dailytrust ta ruwaito.

Rahoton vanguard ya nuna cewa, an kashe yan bindiga da dama yayin wannan aiki na jirgin NAF

Rahotanni sun bayyana cewa harin da jirgin yaƙin ya kai ya kashe wasu makiyaya dake aikin satar shanu, kuma jirgin ya taso ne daga sansanin soji dake jihar Katsina.

Sai dai an gano cewa ɗaya daga cikin bam ɗin da jirgin ya jefa ya dira a wurin taron murnar ɗaurin aure a Wani Ƙauyen jihar Neja, kamar yadda wani shaidan gani da ido ya tabbatar.

Shaidan yace: "Mun hangi wani jirgi na sakin bam a maɓoyar yan bindiga, amma ɗaya daga cikin bam ɗin ya sauka a wurin taron murnar ɗaura aure a ƙauyen Argida."

"Biyu daga cikin mazauna ƙauyen sun mutu, kuma mun gano cewa wasu baƙi da aka gayyato wajen taron sun ji raunuka."

Amma da aka tuntuɓi kakakin rundunar sojin sama, Edward Gabkwet, yace harin bam ɗin da suka gudanar ya tafi yadda ake so cikin nasara.

Yace: "Ba a kawo mana wani rahoton cewa harin ya shafi waɗanda ba ruwan su ba, manufar mu ita ce yan bindigan dake yankin Genu. Bayan mun samu rahoton fasaha cewa sun taru a yankin suna ƙulla shirin kaiwa mutane hari."

Source: Legit.ng

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/L2WpsKOTg5Q6ieoYKEWxeB

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN