Mutane 10 yan gida daya a garin Gwanara a karamar hukumar Baruteen na jihar Kwara sun riga mu gidan gaskiya bayan sun sha wani maganin gargajiya a ranar Juma'a, Daily Trust ta ruwaito.
Abin bakin cikin ya jefa mutanen garin na Baruteen da mafi yawancinsu Fulani ne cikin dimuwa da damuwa.
Ba a samu cikaken bayani game da yadda lamarin ya faru ba a lokacin hada wannan rahoton.
Wasu yan garin da aka yi magana da su a wayan tarho sun ce garin na da nisa sosai daga babban birnin jihar, Leadership ta ruwaito.
A cewarsu, fulanin da abin ya faru da su ba masu yawo bane, asalinsu yan garin Kaiama ne.
Karamar hukuma ta tabbatar da afkuwar lamarin
Da aka tuntube shi, shugaban kwamitin riko na Baruteen, Abdulrashid Ibrahim ya shaidawa Daily Trust cewa ya aika da tawaga a ranar Talata don su yi bincike amma har yanzu ba su dawo ba.
Ya ce:"
Ka san wurin da nisa. Tuni na aika tawaga na jami'an tsaro da masu bada taimako."
Har yanzu safen ranar Laraba, muna jiran dawowarsu.
"Abin da muka sani shine su Fulani ne da suka sha jiko da ake zargin ya kashe dukkansu 10. Idan tawagata ta dawo, za mu yi karin bayani kan lamarin."
Yadda abin ya faru
Rundunar yan sandna jihar Kwara ta bakin kakakinta, Ajayi Okasanmi ta ce wani Ibrahim Bonnie daga rugar Fulani na Biogberu, Gwanara cewa wani Okosi Musa da Worugura Junlin sun zo wurin mahaifiyarsa, Pennia Bonni a rugarsu suka bata maganin ciwon kafa.
Ajayi ya ce:"
Sun kuma umurci ta tabbatar kowa a gidan ya sha maganin domin kada su harbu da ciwon kafar, bayan shan maganin sai suka fara mutuwa daya bayan daya har da mahaifiyar mai ciwon kafan."
Kwamishinan ya sanda, Mohammeed Lawal Bagega ya bada umurnin a yi bincike sannan wadanda ake zargin suna taimakawa rundunar.
Source: Legit Newspaper
https://chat.whatsapp.com/L2WpsKOTg5Q6ieoYKEWxeB
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari