Jami'an sojin Najeriya sun sheke masu safarar makamai guda uku a kauyen Naimaimai da ke kan iyakan Najeriya da jamhuriyar Nijar.
Kakakin hukumar sojin Najeriya Janar Muhammed Yarima ya ce soji sun sheke masu safarar makaman ne ranar Talata daya ga watan Yuni. Ya ce mutanen suna gudanar da kasuwancin makaman ne a yankin Sabon Birni.
Ya ce soji sun kama makamai a lokacin kwanton bauna da suka yi a cikin daji tsakanin dajin Najeriya da jamhuriyar Nijar sakamakon samun ingantaccen bayanan sirri.
Daga cikin makamai da aka kama sun hada da bama baman RPG da chajar su, bindigogi kirar AK47 da wasu na'ukan makamai da albarussai.
Reported by ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari