Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya yi kira ga kamfanin sadarwa na MTN da su rage farashin sayen 'Data' ga yan Najeriya, kamar yadda the cable ta ruwaito.
Buhari yayi wannan kira ne yayin da ya karɓi baƙuncin shugabannin kamfanin, ƙarkashin jagorancin shugaban MTN, Ralph Mupita, a fadar sa dake Abuja.
Buhari ya tabbatar wa kamfanin MTN cewa gwamnatinsa zata yi duk me yuwu wa domin samar da kyakkyawan wuri na yin kasuwanci a Najeriya.
Buhari yace: "Najeriya ce ƙasar da kuka fi samun garabasar kasuwanci a Africa, Asia da sauran su, kuma ita ce ƙasa ta uku da kamfanin MTN yafi samun kuɗin shiga. Sabida haka, muna roƙon ku, ku sauƙaƙa wa yan Najeriya masu amfani da MTN."
MTN yace za'a samu ƙasarancin sabis sabida matsalar tsaro
A ranar laraba, shugaban MTN Nigeria, Karl Toriola, ya bayyana cewa kwastomomi ka iya fuskantar karancin sabis a Najeriya saboda ƙaruwar matsalar tsaro.
Kamfanin sadarwar na MTN ya kara da cewa zai yi iyakacin ƙoƙarinsa ya tabbatar da an samu ingantaccen sabis da zai wa yan Najeriya aiki yadda suke buƙata.
A wani labarin kuma Sojoji Sun Kashe Yan Bindigan da Suka Sace Ɗaliban FGC a Kebbi Sama da 80
Sojoji sun kashe yan bindiga sama da 80, waɗanda suka sace ɗaliban makarantar FGC Birnin Yauri, kamar yadda BBC Hausa ta ruwaito.
Shaidu sun bayyana cewa jami'an sojin sun yi amfani da dabarar yaƙi, inda suka yi wa ɓarayin kofar rago.
Source: Legit Newspaper
https://chat.whatsapp.com/L2WpsKOTg5Q6ieoYKEWxeB
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari