Manomi ya sheke wani makiyayi har lahira saboda kiwo a gonarsa


Wata kotun Magistrate dake Ilorin ta bada izinin a cigaba da tsare wani Manomi mai suna Segun Adebayo Wanda ya harbe wani Makiyayi har lahira a gidan kaso da ke Oke-Kura.

Hukumar yan sandan tana tuhuman Adebayo da laifin kisa.

Mai Sharia Ibrahim Dasuki wanda ya bada izinin haka, Ya dage Zaman sauraro har zuwa June 22 inda zaa cigaba da sauraron karan.

Tun da fari ne, Lauya mai suna Inspekta Zachaues Folorusho lauya Mai kare wanda aka kashe, Ya bayyana ma Kotu cewa Dan uwan Mamacin mai suna Muhammad Adamu ya kawo ma 'yan Sanda rahoton Cewa dan uwansa fa bai dawo daga kiwo ba.

Dan Sanda ya bayyana Cewa wanda ake tuhuma wato Adebayo ya amsa laifin kisan da yayi, A dalilin ya kama Makiyayi yana kiwo a gonar sa.

Folorunsho ya kara bayyana cewa, Wanda ake tuhuma ya amsa laifin shi ya kashe wannan matashi mai Shekara Sha takwas, A inda yayi kokarin boye gawan.

Ya roki Alfarmar kotu data cigaba da tsare Mai laifin domin laifinsa ya fi karfin beli.

Haka zalika Jaridar pulse.ng, ta bayyana cewa wanda ake tuhuma bai yi musu ba ya amsa laifin sa.

Source: Legit

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/L2WpsKOTg5Q6ieoYKEWxeB

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN