Hotuna: Gwamna Bagudu zai shiga daji da mafarautan Kebbi don ceto ɗaliban Yawuri


Gwamnan Kebbi Atiku Bagudu ya ce zai shiga daji domin ceto ɗaliban makarantar garin Yauri da ƴan bindiga suka sace.

Gwamnan ya yi wannan alwashin ne gaban mafarautan jihar Kebbi inda ya ce“Na kira gayya kuma za mu shiga daji.”


Ya kuma faɗa wa mafarautan cewa su tafi su shirya kafin ya yi magana da shugabannin jami’an tsaro. Ya ce an zaɓe su ne ba don su yi zauna a ofis ba,

“Dama Kur’ani aka ba mu mun ka yi rantsuwa kuma ba mu yi rantsuwa ba don mu zauna a ofis ba,” in ji shi.


A ranar Alhamis ne ƴan bindigar suka kutsa Kwalejin Yawuri suka sace ɗalibai da dama.

Jami’an tsaro sun yi nasarar ceto wasu daga cikin ɗaliban, tare da kashe ƴan bindiga da dama.


Rahotanni sun ce an yi gumurzu sosai tsakanin jami’an tsaro da ɓarayin dajin a ƙaramar hukumar Sakaba ta jihar Kebbi.

Rahotun BBC

Hotuna: KBGH

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/L2WpsKOTg5Q6ieoYKEWxeB

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN