Manyan sojoji ashirin da tara aka tirsasa yin murabus daga aiki bayan nada Manjo Janar farouk Yahaya a matsayin shugaban rundunar sojin kasa na Najeriya.
Wannan tirsasa murabus din ya ci karo da ikirarin hedkwatar tsaro na makon da ya gabata wanda suka ce babu sojan da za a yi wa ritaya duk da nada Yahaya a matsayin shugaban sojin kasa da Buhari yayi.
Yahaya mai mukamin Manjo Janar daga jihar Sokoto ya samu mukamin shugaban sojin kasa na Najeriya a ranar 27 ga watan Mayu bayan mutuwar Ibrahim Attahiru.
A wata takarda da Premium Times ta gani, ta nuna cewa an amincewa sojoji masu mukamin manjo janar 29 su tafi hutu, lamarin da zai bude hanyar ritayarsu.
Wannan ritayar ta zo ne kasa da makonni biyu bayan nada Yahaya a matsayin shugaban rundunar.
Ga jerin sunayensu:
1. JB Olawumi
2. JO Akomolafe
3. CO Ude
4. G Oyefesobi
5. MO Uzoh
6. CC Okonkwo
7. MSA Aliyu
8. UM Mohammed
9. BM Shafa
10. NE Angbazo
11. YP Auta
12. SA Yaro
13. J Sarham
14. HE Ayamasoawei
15. OF Azinta
16. BA Akinroluyo
17. KAY Isiyaku
18. AT Hamman
19. AM Aliyu
20. HPZ Vintienagba
21. HR Momoh
22. JR Unuigbe
23. AA Jidda
24. OI Uzomere
25. MH Magaji
26. LA Adegboye
27. MA Masanawa
28. OA Akinyemi
29. AM Dauda
Source: Legit
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari