Duba sunayen manyan soji 29 da rundunar soji ta yi wa ritayar dole bayan nadin COAS


Manyan sojoji ashirin da tara aka tirsasa yin murabus daga aiki bayan nada Manjo Janar farouk Yahaya a matsayin shugaban rundunar sojin kasa na Najeriya.

Wannan tirsasa murabus din ya ci karo da ikirarin hedkwatar tsaro na makon da ya gabata wanda suka ce babu sojan da za a yi wa ritaya duk da nada Yahaya a matsayin shugaban sojin kasa da Buhari yayi.

Yahaya mai mukamin Manjo Janar daga jihar Sokoto ya samu mukamin shugaban sojin kasa na Najeriya a ranar 27 ga watan Mayu bayan mutuwar Ibrahim Attahiru.

A wata takarda da Premium Times ta gani, ta nuna cewa an amincewa sojoji masu mukamin manjo janar 29 su tafi hutu, lamarin da zai bude hanyar ritayarsu.

Wannan ritayar ta zo ne kasa da makonni biyu bayan nada Yahaya a matsayin shugaban rundunar.

Ga jerin sunayensu:

1. JB Olawumi

2. JO Akomolafe

3. CO Ude

4. G Oyefesobi

5. MO Uzoh

6. CC Okonkwo

7. MSA Aliyu

8. UM Mohammed

9. BM Shafa

10. NE Angbazo

11. YP Auta

12. SA Yaro

13. J Sarham

14. HE Ayamasoawei

15. OF Azinta

16. BA Akinroluyo

17. KAY Isiyaku

18. AT Hamman

19. AM Aliyu

20. HPZ Vintienagba

21. HR Momoh

22. JR Unuigbe

23. AA Jidda

24. OI Uzomere

25. MH Magaji

26. LA Adegboye

27. MA Masanawa

28. OA Akinyemi

29. AM Dauda

Source: Legit

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN