Da sanin gwamnati nake shiga daji, babu wanda ya kama ni – Sheikh Gumi


Malamin Musuluncin nan na Jihar Kaduna, Sheikh Ahmad Gumi ya musanta rahotannin da ke cewa hukumar tsaro ta DSS ta gayyata ko ta kama shi domin amsa wasu tambayoyi game da alaƙarsa da 'yan fashin daji.

Shehin malamin ya faɗa wa BBC Hausa cewa "da ma muna da alaƙa" a lokacin da aka tambaye shi ko da gaske ya amsa gayyatar jami'an tsaron.

"Babu wanda ya gayyace ni", in ji shi. Sai dai tun farko mai magana da yawun DSS, Peter Afunaya, ya faɗa wa Channels TV cewa "mun gayyaci malamin domin amsa tambayoyi".

Da yake magana da Channels, Sheikh Gumi ya ce: "Tun sanda na fara shiga daji, ina shiga ne da jami'an tsaro; tare da sanin 'yan sanda da DSS da sarakunan gargajiya da shugabannin Fulani. Ban taɓa shiga ni kaɗi ba."

Kazalika malamin wanda ya sha nema wa 'yan fashin daji afuwa, ya jaddada cewa bai taɓa zargin rundunar sojan Najeriya ba baki ɗayanta da taimaka wa 'yan bindigar da suka addabi jihohin arewa.

Haka nan, an san malamin da shiga dazukan da ke arewacin Najeriya domin yin abin da ya kira wa'azi da faɗakar da 'yan fashin da ke kashe mutane kusan kullum da kuma kama wasu domin karɓar kuɗin fansa.

Rahotun BBC

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/L2WpsKOTg5Q6ieoYKEWxeB

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN