Ana zaman makoki a Zamfara

J

ama'ar garuruwan Magami da Mayaɓa a ƙaramar hukumar Gusau ta jihar Zamfara a arewacin Najeriya, na can su na ci gaba da makoki bayan kisan gillar da 'yan fashin daji suka yi wa mutane a cikin gonakinsu.

Da yammacin ranar Laraba, wani shaida ya ce sun yi wa mutum goma sha bakwai, jana'iza kuma an raunata ƙarin manoma tara, baya ga dabbobi da suka yi awon gaba da su.

Manoman na tsaka da aikin share gonakinsu lokacin da maharan suka auka musu.

Wani da ya tsallake rijiya da baya a harin, wanda ya bukaci a sakaya sunansa, ya shaida wa BBC cewa sun yi jana'izar mutanen da aka hallaka.

Sannan ƴan bindiga sun wawushe musu dukiya da dabobbi. Kuma babu jami'in tsaro lokacin da aka kai musu harin.

BBC ta yi ƙoƙarin jin ta bakin SP Muhammad Shehu, jami'in hulɗa da jama'a na 'yan sandan jihar Zamfara, sai dai haƙarmu ba ta cimma ruwa ba.

Rahotun BBC

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN