Ana cikin rudani yanzu haka a Oshodi da ke birnin Lagos bayan soji sun mamaye muhimman wurare da ke Unguwar. Lamari da ya tsayar da harkokin zirga zingan jama'a a Unguwar man take.
Yanzu haka fasinjoji da magidanta na nan tsaye ba tare da sanin mafita ba sakamakon dakatar da zirga zirga da lamarin ya haifar.
Jaridar Daily Trust ta labarta cewa sojin sun mamaye Unguwar Oshodi ne da sanyin safiyar Alhamis saboda wasu bata gari sun kashe wani hafsan sojin sama a Unguwar bayan sun yi masa duka har ya mutu.
Jaridar ta ce an barnata motocin bas na jigila da yawa kuma sojin sun lallasa wasu fasinjoji.
Lamarin ya rutsa da fasinjoji da ke kan hanyarsu ta zuwa wajen aiki yayin da yara yan makaranta suka ranta a na kare suka koma gida domin guje wa tashin hankalin.
Yanzu haka sojin da ke kai kawo a Unguwar Oshodi suna neman yan iskan da suka kashe hafsan sojin saman a cikin unguwar.
Unguwar Oshodi mahada ce zuwa wasu muhimman unguwanni, kuma nan ne ke da babban tashar motar bas na zirga zirga a Birnin Lagos.
Daily trust ta ce Kakakin hukumar yansandan jihar Lagos Muyiwa Adejobi, bai amsa kiran wayar salula ba kazalika bai mayar da sakon text da aka yi mata akan lamarin ba.
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari