Ƴan bindiga sun kashe ƴan sa-kai 19 a ƙauyen Yartsakuwa a ƙaramar hukumar Rabah na jihar Sokoto kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Wani mazaunin garin, wanda ya yi magana da majiyar Legit.ng a wayar tarho ya ce ƴan sa-kan sun rasa rayukansu ne yayin da suke ƙoƙarin daƙile harin da ƴan bindigan suka kaiwa garin.
Mazaunin garin, da ya nemi a ɓoye sunansa ya ce yan bindigan sun kai hari ne ƙauyen misalin ƙarfe ɗaya na ranar Lahadi.
"Sun zo ne da nufin kashe ɗaya daga cikin shugabannin ƴan sa-kan a yankin," in ji shi.
An ruwaito cewa ƴan bindigan sun halaka shugaban ƴan sa-kan (da aka ɓoye sunansa) a gonarsa.
Kansilar Ghandi A, Aminu Mua'azu Ghandi shima ya tabbatar da afkuwar lamarin lokacin yana mai cewa 14 cikin yan sa-kan ƴan Ghandi ne sauran biyar ɗin kuwa ƴan wasu garuruwa ne da ke karkashin Ghandi.
Ya ce wasu mutum 5 da aka yi wa munanan rauni a harin suna asibiti ana musu magani
Ya kara da cewa yan bindigan sun sace dabbobi da dama da yanzu ba a tantance adadinsu ba.
Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar, ASP Sanusi Abubakar, yayin tabbatar da harin ya ce mutum 10 ne kawai suka mutu cikin ƴan sa-kan.
A cewarsa, yan bindigan sun so shiga ƙauyen Yartsakuwa amma aka dakile harin.
Ya ce bayan yan sa-kan, babu wani mahaluki da aka kashe a garin.
Ya shawarci ƴan sa-kan su rika jiran ƴan sanda kafin su tunkari ƴan bindigan.
Source: Legit.ng
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari