Iyayen daga cikin daliban da aka sace na Kwalejin Nona da Ilimin Gandun Daji ta Tarayya sun yi watsi da ikirarin da ke cewa an yi fyade ga ’ya’yansu ta hanyar lalata da luwadi a tsawon kwanaki 56 da suka kwashe a hannun 'yan bindiga.
Ku tuna cewa a ranar 11 ga watan Maris, 2021, 'yan bindiga sun mamaye kwalejin da ke Afaka a kan titin filin jirgin saman Kaduna suka sace dalibai 39.
Iyayen sun ce babu wani daga cikin ’ya’yansu (daliban) da 'yan bindigan suka yi lalata da su. 'Yan bindigan sun nemi a ba su N500m kudin fansa kafin su sake su.
Iyayen daliban da aka sako sun bayyana cewa tunanin lalata da daliban da daya daga cikin 'yan bindigan yayi shine yasa aka harbe shi har lahira.
Wannan ya na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Shugaban kungiyar Iyaye, Malam Abdullahi Usman ya fitar a Kaduna ranar Lahadi, a Rahoton Reuben Abati.
Sanarwar ta ce, “Mun bayyana karara cewa babu daya daga cikin 37 din da aka sace (wanda aka sako yanzu) na daliban Afaka da 'yan bindiga suka yi lalata da su ko kuma luwadi.
“Don tabbatarwa, daliban sun yi ikirarin cewa 'bai ma gwada hakan da gaske ba; yana fada ne kawai, amma duk da haka an kashe shi kuma an bukaci mu dauki gawarsa mu jefar a wani daji dake kusa saboda sun ce bai cancanci a binne shi yadda ya kamata ba.
“A matsayinmu na iyayen daliban da aka sako, babban abinda muka maida hankali a kai yanzu shi ne gyara 'ya'yanmu da Allah ya dawo mana da su a raye kuma abin mamaki ba a cutar da su ba.
Source: Legit
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Rubuta ra ayin ka