Zanga-zanga ta barke a safiyar ranar Juma'a a garin Zurmi, hedkwatar karamar hukumar Zurmi a jihar Zamfara saboda yawaitar hare-haren yan bindiga da ke kashe mutane a garuruwa kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Mutane da dama sun rasa rayyukansu wasu daruruwan sun rasa muhallansu sakamakon hare-haren yan bindiga da ya ki-ci ya-ki-cinyewa a garuruwan jihar.
A makon da ta gabata, yan bindiga sun kai hari a wani gari a karamar hukumar Zurmi inda suka kashe fiye da mutane 11.
Mazauna garin sun shaidawa majiyar Legit.ng garuruwa da dama a yankin na fuskantar barazana daga yan bindiga.
Sun dauko wasu gawarwakin sun shiga gari suna zanga-zanga nuna damuwarsu kan hare-haren da yan bindiga ke kai musu.
Wani daga cikin mazauna garin da ya ce sunansa Mustapha ya ce: "Suna hanyarsu zuwa fadar sarki domin gabatar da kokensu.
"Sai dai, Sarkin bai fito ya gana da su ba domin an ce yana cikin gida. Sun yi kone-kone a kafin suka tafi.
"Masu zanga-zangan sun bar fadar sunnan suka hadu a hanyar Gusau zuwa Jibia suka fara fasa motoccin matafiya da ke bin titin.
"Sun kuma fasa gilasan motoccin da aka ajiye a gefen titi."
"Yanzu abubuwa sun dai-daita a yayin da jami'an tsaro ke sintiri a titunan garin domin tabbatar da doka da oda.
"Sannan mutane sun koma sun cigaba da harkokinsu kamar yadda suka saba," in ji shi.
Source: Legit Newspaper
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari