Yansanda sun kama wani mutum mai suna Musilumu Mbwire, bisa zargin kashe 'ya'yansa biyu saboda dalilan tsafi a kauyen Jiira da ke Bbaale a gundumar Kayunga a kasar Uganda.
Kwararrun yansanda sun tone gawar daya daga cikin yaran mai suna Latif Kamulasi dan shekara 7, ranar Talata 13 ga watan Mayu. Sai dai har yanu ba a gan gawar daya yaron mai suna Sahum Baizambona dan shekara 3 ba. Har yanzu yansanda na ci gaba da bincike.
Mahaifin yaran ya gaya wa yansanda lokacin bincike cewa ubangidansa a wajen aiki shi ne ya bukaci ya kashe yaran cewa zai bashi Shi4m wattau kudin kasar Uganda Shilin miliyan 4 da gida.
Ya ce uban gidansa ya ce zai yi amfani da jinin yaran ne domin wata bukata. Sakamakon haka mahaifin yaran ya yi masu yankan rago.
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari