Hukumar Hisbah a jihar Kano ta kori wani babban jami'inta bayan zargin kama shi tare da wata matar aure a wani dakin Otal a Unguwar Sabon Gari da ke Kano.
An kama jami'in mai suna Sani Rano a yanayi da ya haifar da zargi a dakin Otal tare da wata mata ranar Talata 16 ga watan Fabrairu 2021.
Sai dai a wata hira da SaharaReporters jami'in sadarwa na hukumar Nabahan Usman ranar Talata 10 ga watan Maris, ya ce jami'in da ake zargi baya da laifi, domin matar da aka same shi tare da ita a dakin wannan Otal diyarshi ce.
Sai dai Kakakin hukumar Hisbah na jihar Kano Lawal Fagge ya tabbatar wa Jaridar Vanguard da korar babban jami'in hukumar da ake cece kuce a kansa ranar Talata 4 ga watan Mayu.
Rahotanni sun ce hukumar ta dauki matakin korar jami'in ne bisa shawarar rahotun Kwamiti da hukumar ta kafa domin binciken lamarin.
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari