Gida ya rufta kan iyalin dansanda, diya ta mutu, uwa da kanwa sun suma


Wata yarinya mai suna Peace Bulus ta mutu bayan sashen gidan da take ciki ya rufta a kanka kuma ya karya hannun yar' uwarta a barikin yansandan dawaki da ke Ikeja a birnin Lagos ranar Talata 4 ga watan Mayu.

Mariganyar tana barci tare da mahaifiyarsu mai suna Hauwa tare da kannenta guda uku, sai ginin ya rufta masu, nan take bungun da ke kofa ya fada kan Peace ya watse kanta.

Mahaifiyar tare da sauran yara sun suma bayan karewar hannun yaruwar Peace. An garzaya zuwa Asibitin yansanda da ke Ikeja da uwarsu Hauwa tare da diyarta bayan sun suma domin samun kulawan Likitoci.

Rahotanni sun ce rundunar yansandan jihar Lagos bata fitar da jawabi kan lamarin ba kawo yanzu.



Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN