Wata yarinya mai suna Peace Bulus ta mutu bayan sashen gidan da take ciki ya rufta a kanka kuma ya karya hannun yar' uwarta a barikin yansandan dawaki da ke Ikeja a birnin Lagos ranar Talata 4 ga watan Mayu.
Mariganyar tana barci tare da mahaifiyarsu mai suna Hauwa tare da kannenta guda uku, sai ginin ya rufta masu, nan take bungun da ke kofa ya fada kan Peace ya watse kanta.
Mahaifiyar tare da sauran yara sun suma bayan karewar hannun yaruwar Peace. An garzaya zuwa Asibitin yansanda da ke Ikeja da uwarsu Hauwa tare da diyarta bayan sun suma domin samun kulawan Likitoci.
Rahotanni sun ce rundunar yansandan jihar Lagos bata fitar da jawabi kan lamarin ba kawo yanzu.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari