Mayakan kungiyar Boko Haram sun cinna wuta a wasu a gidaje a Maiduguri, babban birnin jihar Borno, Daily Trust ta ruwaito.
Ana kuma jin karar harbin bindiga da abubuwa masu fashewa a sassan birnin daban-daban musamman kusa da Jiddari Polo.
Majiyar Legit.ng ta ruwaito cewa ana musayar wuta tsakanin sojoji da wasu da ake zargin yan ta'adda ne a kusa da Molai da Jiddari a babban birnin jihar.
"An ji a kalla karar abin fashewa uku a Maiduguri. Ana harbe-harben bindiga a halin yanzu, farar hula suna tserewa daga gidajensu suna tafiya hanyar Damboa da tsohuwar GRA," a cewar majiyar tsaro.
Wani mazaunin garin da ya yi magana da majiyar Legit.ng a wayar tarho ya ce bashi da wurin zuwa a halin yanzu saboda halin da ake ciki.
"A yanzu babu inda zan iya tafiya. Ba zan iya zuwa gida ba. Kana iya jin karar harbin bindigan?" in ji shi.
'Yan ta'addan sun kai harin ne a daidai lokacin da musulmi ke shirin yin bude baki a cikin watan Ramadan mai albarka.
Daga bisani, zaratan dakarun sojoji sun fatattake yan ta'addan amma a halin yanzu ba a kiyasta adadin barnar da yan ta'addan suka yi ba.
Source: Legit.ng
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari