Da dumi-dumi: Jami'an Tsaro sun dakile sabon hari da aka kaiwa Ofishin ‘yan sanda na Imo, sun kashe yan daba 8


Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba a daren Alhamis, 6 ga Mayu, sun yi yunkurin kai hari Hedikwatar’ Yan sanda ta Orlu a jihar Imo.

Jami'an tsaro a wani aikin hadin gwiwa, sun dakile harin kuma sun kashe akalla mutane takwas daga cikin maharan, jaridar The Punch ta ruwaito.

Legit.ng ta tattaro cewa sun kuma kwato motoci bakwai da maharan suka shigo domin ta’asar.

An tattaro cewa an shafe tsawon awanni ana musayar wuta tsakanin ‘yan bindigar da jami’an tsaron.

Artabun ya haifar da firgici yayin da mutane suka rarrabu don kare kansu lamarin da ya sa hanyoyin da ke cikin garin Orlu da kewayensa zama tsit.

Da take bayar da rahoton faruwar lamarin, jaridar The Nation ta bayyana cewa ba a samu jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar ba amma wani babban dan sanda da ba a ambaci sunansa ba ya tabbatar da ci gaban.

An rahoto cewa babban jami’in dan sandan ya ce an tafi da gawarwakin ‘yan fashin da motocin zuwa hedikwatar rundunar ‘yan sanda da ke Owerri.

Ya bayyana cewa ba a kona hedkwatar rundunar 'yan sanda ba kuma ba a kashe kowani jami'in tsaro a harin ba.

A gefe guda, ana fargabar mutane biyu sun rasa rayukansu bayan wasu mutane dauke da makamai sun kai hari kan motar banki a kauyen Elemosho da ke kan babbar hanyar Akure-Ondo a karamar hukumar Ondo ta Gabas ta Ondo da yammacin ranar Alhamis.

Wadanda suka shaida lamarin sun ce ‘yan bindigan sun zo ne a cikin wata motar Lexus, kuma suka afka wa motar da ke kan hanyar zuwa Akure da misalin karfe 5 na yamma sannan suka yi awon gaba da wasu kudade da ba a bayyana yawansu ba.

Source: Legit


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN