Rundunar yansandan jihar Ogun ta kama wani Lauyan bogi Dan shekara 50 mai suna Azeez Agboola ranar Laraba 31 ga watan Maris yayin da yake tsakar kare shari'a a gaban Alkali a cikin Kotu.
Lauyan wanda ke zaune a unguwar Oko Afir da ke Badagry a Birnin Lagos, ya bayyana ne a gaban mai sharia B.I. Ilo na Kotun Majistare da ke Agbara domin kare wata sharia da ke gaban Alkalin.
Sai dai yadda ya gabatar da kansa da kuma tafiyar da bayani a gaban Alkali ya haddasa wa Alkalin shakku ko shi cikakken Lauya ne. Sakamakon haka Alkalin ya kira yansanda domin su tantance ko ainihin Lauya ne shi.
Sai dai bayan yan sanda sun gayyace shi kuma suka yi masa tambayoyi, Lauyan ya shaida wa yansanda cewa tabbas ya karanci Law, amma bai ci jarabawan karshe ba sakamakon haka ba a kira shi zuwa makarantar koyon aikin Lauya ba da ake kira Bar.
Yansanda za su gurfanar da shi a gaban Kotu da zarar sun kammala bincike. A cewar Kakakin yansandan jihar Ogun DSP Abimbola Oyeyemi wacce ta tabbatar da labarin.
https://chat.whatsapp.com/Cw2uhGNZiIzGM88PV4gpOI
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari