Rundunar yansandan jihar Ekita ta kama wata mata mai suna Joy Fatoba, sakamakon kulle tagwayenta masu shekara 3 a cikin daki har tsawon kwana 3 ba tare da basu abinci ko ruwan sha ba.
Kakakin rundunar yansandan jihar Ekiti Sunday Abutu, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata takarda da ya fitar ranar Litinin 5 ga watan Maris. Ya ce yansanda sun ceto yaran kuma sun kai su Asibiti domin samun kulawan Likitoci .
Abutu ya ce ranar Lahadi 4 ga watan Aprilu yansanda sun sami kira daga karamar hukumar Igbara-Odo, Ekiti ta kudu maso yamma a jihar Ekiti cewa wata mata ta kulle yaranta a cikin daki har tsawon kwana 3 ba tare da basu abinci ko ruwan sha ba.
Ya ce matar ta yi barazanar cewa za ta kashe yaran idan aka tilasta ta bude kofar.
Sai dai rahotanni sun ce matar ta yi zargin cewa tun lokacin da ta dauki cikin yaran, mahaifinsu ya yi tafiyarsa, har ta haihu bai dawo ba. Ta ce yanzu haka lamurra sun yi mata tsauri tare da kuncin rayuwa sakamakon rashin ci gaba a sana'ar kitso na Saloon da take yi wanda da shi ne take samun kula da yaran.
Kazalika rahotanni sun ce ala tilas yansanda suka kai yaran Asibiti bayan an bude daki da mahaifiyarsu ta kulle su domin sun kasa tsayuwa a kafafunsu sakamakon yunwa da kishin ruwa.
https://chat.whatsapp.com/Cw2uhGNZiIzGM88PV4gpOI
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari