Wani matashi ya kashe Kakarshi kuma ya gundule kanta ya saka a cikin laida ya kai ofishin yansanda na Kisumu a kasara Kenya ranar 5 ga watan Aprilu.
Wannan lamari ya haifar da mamaki tsakanin yansanda. Sai dai yansanda sun dauki saurayin a cikin motocinsu suka tafi rukunin gidajen Nyalenda inda saurayin ya kashe tsohuwar.
Yansanda sun dauki gawar tsohuwar suka kai dakin ajiye gawa a Asibiti domin gudanar da binciken Postmortem, yayin da suka damke saurayin kuma suka ci gaba da gudanar da bincike.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/Cw2uhGNZiIzGM88PV4gpOI
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari