PDP ta ce ba ta dakatar da Kwankwaso ba


Babbar jam'iyyar adawa a Najeriya PDP ta musanta wata takarda da ke yawo a kafafen sada zumunta wadda ke cewa jam'iyyar ta dakatar tsohon gwamnan Kano Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso da takwaransa Babangida Aliyu na jihar Neja.

Cikin wata sanarwa da PDP ta fitar a shafinta na Twitter ta ce, akwai wasu ka'idoji da kundin tsarin jam'iyyar ya tanada gabanin dakatar da duk wani mamba.

PDP ta ce ba za ta amince da irin wadannan karyace-karyacen ba, wadanda za su iya kawo hargitsi cikin jam'iyyar ko kuma su haifar da rikici tsakanin mambobinta.

Haka kuma ta musanta dakatar da tsohon gwamnan jihar Neja Babangida Aliyu tana cewa duka bayanan da aka fitar na dakatar da shi basu da tyshe bare makama.

Others
Image caption: PDP ta ce ta ba san daga ina wannan takaradr ta samo asali ba

Jam'iyyar ta shawarci shugabanninta a jihohin Kano da Neja da su hada kai wuri guda su kuma yaki irin wadannan bayanan da za su iya kawo rabuwar kai, a lokacin da 'yan Najeriya ke bukatar jam'iyyar.

Rahotun B C Hausa


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/Cw2uhGNZiIzGM88PV4gpOI

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN